1. Tsallake zuwa shafin jadawali
  2. Tsallake zuwa jadawalin abubuwan da shiri ya kunsa
  3. Tsallake zuwa karin wasu shafukan DW

UNESCO ta karrama 'yan jaridun yankin Falasdinu

May 3, 2024

Albarkacin ranar 'yancin jarida ta duniya, Hukumar UNESCO ta ba da kyautar karramawa ta shekara-shekara ga 'yan jaridun yankin Falasdinu da suka share watanni suna aiki cikin yanayin yaki.

https://p.dw.com/p/4fSPF
UNESCO ta bai wa 'yan jaridun Gaza lambar yabo
UNESCO ta bai wa 'yan jaridun Gaza lambar yaboHoto: Momen Faiz/NurPhoto/picture alliance

Hukumar ilimi da kimiya da raya al'adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO ta bayar da lambar yabo ta 'yancin 'yan jaridu ga daukacin 'yan jaridar yankin Falasdinu da ke aikawa da rahotanni daga zirin Gaza wanda ya shafe sama da watanni shida cikin kazamin yaki sakamakon farmakin da Isra'ila ta kai a kudancin yankin.

A lokacin da yake sanar da wannan karramawa, shugaban alkalan da suka jagoranci tantance bayar da lambar yabon Mauricio Weibel ya yi jinjinar ban girma tare da karfafa gwiwa ga 'yan jaridar yankin Falasdinu da suka jajirce wajen gudanar da aikinsu duk da hadarin da suke fuskanta cikin yanayi na yaki.

Karin bayani: 'Yancin 'yan jarida ne yancin duniya

Daga nata bangare darekta janar ta Hukumar UNESCO Audrey Azoulay ta jaddada muhimmancin hada kai ta yadda 'yan jaridu a fadin duniya za su ci gaba da gudanar da aikinsu cikin 'yanci da adalci.

Karin bayani: UNESCO: 'Yan jaridar da ake kashewa na karuwa

A cewar kungiyar kare hakkin 'yan jarida da ake wa lakabi da CPJ mai hedikwata a birnin New York na Amurka, akalla 'yan jarida da ma'aikatan yada labarai 97 ne aka halaka daga farkon yakin Gaza zuwa wannan lokaci, kuma 92 daga cikinsu Falasdinawa ne, yayin da wasu 16 suka jikkata.